Cibiyar kula da lafiyar Gwamnatin Najeriya da ke birnin Yolan Jihar Adamawa a yankin arewa maso gabashin kasar ta yi nasarar aikin raba wasu tagwaye da aka haife su manne da juna a kirji. Wannan dai babbar nasara ce ga fannin lafiyar Najeriyar, la'akari da cewa a baya sai an fitar da irin wadannan jarirai kasashen ketare kafin yi musu Tiyata.
