Bola Ahmad Tinubu jagoran jam’iyar APC na kasa da kuma shugaban jam’iyar, John Odigie Oyegun na daga cikin mutanen da suka halarci wata liyafar cin abinci da shugaban kasa Muhammad Buhari ya shirya a ranar Laraba.
An fara taron liyafar da misalin karfe 8:30 na dare a babban dakin taro na Banquet dake fadar shugaban kasa.
